Kamfanin dillancin labaran kasa da kasa na Ahlul-Baiti (A.S) - ABNA - kakakin Kungiyar Rundunar Hizbullah Iraki ya ce: Dagewar da Al-Saud ta yi na kulla yarjejeniyoyin sulhu da kuma nutsar da su a cikin tarkacen bauta da cin amana ba zai bude musu kofofin goyon bayan kasashen yamma ba, sai dai zai bude musu kofofin tsinuwa da kin amincewa da Gwagwarmaya.
Tunkarar gwagwarmayar Musulunci ita ce hanya daya tilo ta 'yantar da kasarmu daga mamayar kasashen waje, kuma ba mu yarda da kasancewar sojojin kasashen waje musamman sojojin Amurka da na Turkiyya a Iraki ba.