Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ابنا
Alhamis

27 Yuli 2023

10:02:45
1382751

Sojoji Sun Sanar Da Hambarar Da Gwamnatin Jamhuriyar Nijar

Wasu gungun sojoji a Nijar sun sanar hambarar da gwamnatin shugaban kasar Mohamed Bazoum da rufe kan iyakokin kasar da kuma sanya dokar hana fitar dare.

Kamfanin dillancin labaran shafin sadarwa na yanar gizo na Ahlul-Baiti (A.S) - ABNA - ya nakalto maku daga Tashar Hausatv da ke Iran cewa, Wasu gungun sojoji a Nijar sun sanar hambarar da gwamnatin shugaban kasar Mohamed Bazoum da rufe kan iyakokin kasar da kuma sanya dokar hana fitar dare.

Manjo Amadou Abdel Rahman ya bayyana cewa: Su jami'an tsaro da jami'an tsaro sun karbe madafun ikon kasar tare da yanke shawarar dakatar da dokokin mulkin Nijar, sakamakon ci gaba da tabarbarewar sha’anin tsaro da tabarbarewar tattalin arziki da zamantakewar kasar.


Abd al-Rahman ya jaddada cewa: Majalisar mulkin sojin kasar zata mutunta duk wasu yarjeniya da Nijar ta dauka, yana mai fayyace cewa; Majalisar zata mutunta dokokin kasa da kasa da amincin tsigaggen shugaban kasar kamar yadda ka’idojin kare hakkin dan Adam suka shimfida.


Sanarwar gungun sojojin da suka gudanar da juyin mulkin ta yi nuni da cewa: Da dakatar da duk wasu cibiyoyi da suka fito daga tsohuwar jamhuriya ta bakwai da ta gabata, sannan manyan sakatarorin ma'aikatun ne za su dauki nauyin gudanar da harkokin ayyukan ofisoshin, jami'an tsaro ne zasu tafiyar da sauran al’amura, kuma suna bukatar takwarorin hulda da Nijar na kasashen waje da kada su dauki matakin tsoma baki a harkoki cikin gidan kasar.