Kamfanin dillancin labaran shafin sadarwa na yanar gizo na Ahlul-Baiti (A.S) - ABNA - ya habarta cewa, Sojojin Isra'ila sun shiga birnin Nablus da ke gabar yammacin kogin Jordan a ranar Laraba (a daren jiya) don lalata gidan "Usame Tawal", wani fursuna dan kasar Falasdinu wanda yake jami'in dakarun gwagwarmaya ne, inda shigar ta su ta haifar da rikici da Falasdinawan.
A cewar jaridar Yediot Aharonot akalla Bafalasdine daya ya mutu sakamakon musayar wuta da aka yi tsakanin bangarorin biyu, sannan wasu Falasdinawa uku sun jikkata.