Kamfanin dillancin labarai na Ahlul Bait (a.s) ABNA ya bada cewa, wani dan kasar Yemen ya rasa ransa, yayin da wasu goma suka jikkata a jiya Talata, sakamakon luguden wuta da dakarun kawancen Saudiyya suka yi a gundumar Munabbih da ke lardin Sa'ada a arewacin kasar Yemen.
Tashar talabijin ta Al-Masirah ta kasar Yemen ta rawaito cewa, sojojin Saudiyya sun bude wuta kan gidajen 'yan kasar, kauyuka, da shaguna a yankin Al-Raqo na gundumar Munabbih da ke kan iyaka, inda suka kashe wani dan kasar tare da jikkata wasu 10, ciki har da wasu bakin haure 'yan Afirka biyu. .
A shekaran jiya litinin wasu ‘yan kasar 4 ma sun jikkata sakamakon harin bom din da dakarun kawancen da Saudiyya ke jagoranta inda suka kai a wasu yankuna daban-daban na gundumar Shada da ke kan iyaka da jihar Sa’ada.
A 'yan kwanakin da suka gabata ma dai wani farar hula dan kasar Yaman ya mutu sakamakon Bude wuta da kawancen da Saudiyya ke jagoranta ya yi a yankin Al Thabet da ke gundumar Sa'ada da ke kan iyakar Qatar kamar yadda wata majiyar gwamnati a birnin San'a ta tabbatar.
Wani abin lura da cewa, a kullum, ana fuskantar hare-hare a yankunan kan iyaka da ke cikin gundumar Saada, a kullum ana ci gaba da kai hare-hare ta hanyar harba makamai masu linzami da harsasai da kuma kai hare-hare kan fararen hula, lamarin da ke haddasa mace-mace da jikkata.