Kamfanin dillancin labaran Ahlul-Baiti (a.s) - ABNA - ya kawo rahoton cewa: Ayatullah Sheikh Isa Qassim ya tabbatar da cewa: al'ummar musulmi ne ke da alhakin mayar da martani kan harin da yahudawan sahyuniya suka kai a kan masallacin Al-Aqsa.
Sheikh Qassim ya tabbatar da hakan a shafinTwitter a shafinsa na Tuwita cewa "dukkan al'ummar musulmi a bisa sharia ne ke da alhakin dakile mamayar Isra'ila tare da kin barin yahudawan sahyoniya su ci gaba da kai farmaki kan masallacin Al-Aqsa."
Kuma ya yi gargadin cewa "ketara iyaka da yahudawan sahyuniya suke yi wa Al-Aqsa da musulmin da suke zaune a cikinsa suke Iitikafi, tamkar tauye martabar masallacin ne, da keta alfarmar Musulunci da yaki da bautar Allah."