Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Iran: Harin da aka kai kan masallacin Al-Aqsa wani lamari ne da ke nuni da kyamar bil'adama na gwamnatin sahyoniyawa.
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Hare-haren wuce gona da iri da sojojin yahudawan sahyoniyawan suka yi wa masu ziyara da masu ibada a masallacin Al-Aqsa, ya sake bayyana irin ta'asar da wannan gwamnatin take aikatawa a gaban idanun al'ummar Palastinu a duniya."