Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ابنا
Lahadi

19 Faburairu 2023

12:35:07
1347362

Kaskancin na kasa da kasa ga yahudawan sahyoniya

An kori tawagar gwamnatin sahyoniyawan daga taron kungiyar tarayyar Afrika

Kafofin yada labaran Isra'ila sun ce an kori 'yan tawagar wannan gwamnati da ta je Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha domin halartar taron kungiyar Tarayyar Afirka a matsayin 'yan kallo, daga zauren taron karkashin jagorancin jami'an tsaro.

Kafofin yada labaran Isra'ila sun ce an kori 'yan tawagar wannan gwamnati da ta je Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha domin halartar taron kungiyar Tarayyar Afirka a matsayin 'yan kallo, daga zauren taron karkashin jagorancin jami'an tsaro.


Jaridar "Haaretz" ta bayyana korar 'yan Isra'ila daga wannan taro a matsayin wani abu da ba a saba gani ba a taron kasa da kasa.


Mambobin tawagar yahudawan sahyoniya sun shaidawa Haaretz cewa kasashen Afirka ta Kudu da Aljeriya ne ya sa aka kore su daga wannan taro.