Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ابنا
Lahadi

19 Faburairu 2023

10:51:21
1347350

Zargin Aliyev ga Iran dangane da harin da aka kai ofishin jakadancin Azarbaijan a Tehran

Shugaban kasar Azarbaijan Ilham Aliyev, a wunkurin tafiyarsa zuwa Jamus da kuma halartar taron tsaro na Munich, ya sake nanata ikirarinsa na cewa harin da aka kai kan ofishin jakadancin kasar a Tehran harin ta'addanci ne, inda ya bukaci a gudanar da bincike na gaskiya tare da hukunta wannan mutum da kuma shari'ar mutanen da Ya ce sun aiko shi ne don yin haka.

Shugaban kasar Azarbaijan Ilham Aliyev, a wunkurin tafiyarsa zuwa Jamus da kuma halartar taron tsaro na Munich, ya sake nanata ikirarinsa na cewa harin da aka kai kan ofishin jakadancin kasar a Tehran harin ta'addanci ne, inda ya bukaci a gudanar da bincike na gaskiya tare da hukunta wannan mutum da kuma shari'ar mutanen da Ya ce sun aiko shi ne don yin haka.



Game da lamarin, ya shaida wa manema labarai cewa: A cikin mintuna 30-40 da wannan dan ta'addan na cikin ofishin jakadancin, bai kwance damara ba. A wannan lokacin ne jami’an tsaro da motocin ‘yan sanda suka zo suka tafi, amma sai suka ba wa wannan mutum damar shiga ofishin jakadanci har sau biyu ya kashe jami’in tsaron mu daya tare da raunata wasu biyu. Idan ba don jarumtakar daya daga cikin ma'aikatan wannan ofishin jakadancin ba, mai yiwuwa wannan dan ta'adda ya kashe wasu da dama ma.