Alhuthi ya bayyana hakan ne a yau a cikin wani jawabi wanda ya gabatar da aka watsa kai tsaye a kafofin yada labaran kasar Yemen.
Ya ce tun kafin wannan lokacin Amurka ta yi ta hankoron ganin ta haifar da matsaloli a Yemen, wanda hakan zai bata damar mamaye kasar cikin sauki, amma hakan bata samu, sakamakon tsayin daka al’ummar kasar suka yi.
Ya ci gaba da cewa, gazawar Amurka ce ta sanya ta yin amfani da karnukan farautarta na yankin, domin su aiwatar da manufofinta na ruguza kasar Yemen.
342/