Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto Ahmed Abulgaid babban sakataren kungiyar kasahen larabawa yana fadar haka a birnin Alkahira inda cibiyar kungiyar take.
Babban sakataren ya kara da cewa mutanen kasar Iraki sun sha wahalhalu da dama, kowa yana son ganin kasar ta sami nutsuwa a bangaren siyasa tattalin arziki da kuma tsaron kasar.
A cikin watan Octoban shekarar da ta gabata ce aka gudanar da zaben majalisar dokokin kasar Iraki amma har yanzun an kasa kafa gwamnati a kasar saboda sabanin siyasa a tsakanin yan siyasar kasar.
342/