Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kamfanin dillancion labaran WAFA na gwamnatin Falasdinawa yana fadar haka, ya kuma kara da cewa abin ya faru ne bayan da tawagogin sojojin yahudawan tare da rakiyar motocin yaki da buldozoji kimani 100, suka farwa garin sun kuma rufe kofar shiga da fita daga garin a safiyar yau Talata.
Shugaban babbar asbitin Jenin ya bayyana cewa musayar wuta tsakanin bangarorin biyu ne ya yi sanadiyyar shahadar Muhammad Musa dan shekara 29 a duniya da kuma raunata wasu da dama.
342/