Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Talata

6 Satumba 2022

19:43:35
1304145

Iran Ta Bayyana Kasancewar Isra’ila A Yankin Gabas Ta Tsakiya A Matsayin Haramtacce

Kwamandan hasoshin soji na kasar Iran Major Janaral Mohammar Bageri ya yi tir da ci gaba da kasancewa Isra’ila a yankin gabas ta tsakiya tare da bayyana shi a matsayin haramatacce , domin babu abin da tak jawowa sai rashin tsaro a yankin.

Baqiri ya kara da cewa kasahen yankin gabas ta tsakiya sune ya kamata su samar da tsaro a yankin, don haka babu bukatar sojojin wata kasar a cikin ruwan kasa da kasa, yace Ayyukan da sojojin Isra’ila ke aiwatarwa a yankin shi ne ummul habaisin duk wani rashin tsaro da ake fuskanta, kuma ya gargardi kasashen yankin game da wani sakaci na bada dama ga Isra’ila ta sanya kafarta a yankin

Ana sa bangaren kwamandan dakarun sojojin ruwa na kasar Iran Real Admiral Alir riza Tangsiri a watan jiya yayi gargadi game da duk wani hadin guiwa da gwamnatin Isra’ila na haifar da wata barazana da rashin tsaro a yankin tekun fasaha.

Wanna yana zuwa ne adaidai lokacin da dakarun sojin ruwa na kasar iran suka kaddamar da wani jirgin ruwa na yaki da aka kera a cikin gida da aka bashi suna da shahid Qasim Sulaimani babban kwamandan yaki da ta ‘adancin na kasa iran .

342/