Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Litinin

5 Satumba 2022

17:04:12
1303768

​Iran Tana Iya Magance Karancin Makamashi A Turai Idan An Fahinci Juna A Tattaunawar Vienna

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa idan an fahinci juna tsakanin kasashen Amurka da Turai a bangare guda da kuma kasar Iran a tattaunawar farfado da yarjeniyar JCPOA kan shirin nukliyar kasar, Iran tana iya magance matsalar karancin makamashin da kasashen Turai suke fama da shi.

Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto Nasir Kan’ani kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran yana fadar haka a safiyar yau a taro da kafafen yada labarai da ya saba gabatarwa a ko wace ranar litinin.

Kan’ani ya kara da cewa manufar kasar Iran a farfado da yarjeniyar JCPOA ita ce ganin an Amurka ta soke dukkan takunkuman tattalin arzikin da ta dorawa kasar da kuma mutanen kasar, tare da wasu sharudda, wadanda da su ne Iran zata amfana da yarjejeniyar.

Yace an gabatar da shawarori da dama kuma daga dukkan bangarorin biyu, amma a halin yanzu Iran ta gabatar da ra’ayinta dangane da shawarorin da kasashen Turai suka gabatar, a halin yanzu muna jiran gwamnatin Amurka ta gabatar da ra’ayinta na karshe.

342/