Lauyoyin da ke wakiltar dan takarar shugaban kasar, Raila Odinga sun gabatar da kararsu na neman soke nasarar da mataimakin shugaban kasar William Ruto ya samu a zaben shugaban kasar.
Kwamitin alkalai bakwai ne ke sauraren karar da madugun ‘yan adawa na kasar ya gabatar yana mai kalubalantar sakamakon zaben.
A halin yanzu, ana bincike da sake kirga kuri'u a rumfunan zabe 15 da ake korafi akan sahihancin sakamakon su.
Nan da ranar 5 ga watan Satumban nan da muka shiga ne ake sa ran yanke hukunci.