Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Laraba

31 Agusta 2022

19:31:42
1302245

Iran Ta Na Bukatar Lamuni Daga Amurka Don Farfado Da Yarjejeniyar Nukiliya

Ministan harkokin wajen kasar Iran Amir Abdollahian yayi wannan bayani a yau laraba a taron manema labarai da suka tsakaninsa da takwaransa na kasar Rasha Sergey Lavrov a birnin Mosko ya kara da cewa mun karbi masar Amurka ta karshe kuma muna nazari akansa , don Iran na bukatar lamuni mai karfi daga Amurka a ci gaba da kokarin da ake yi na kawo karshen tattaunawar da ake yi na cirewa Iran takunkumi a kasar Austeriya,

Kasar Amurka ce ta kawo cikas a harjejeniyar da aka cimma a shekara ta 2015 , bayan da ta fice ba tare da wani dalili ba a shekara ta 2018 tare da sake kakabawa iran takunkumi mafi muni duk da hadin kai da iran ta bayar game da dukkan abubuwan da aka cimma yarjejeniya a kai.

Kungiyar Tarayyar Turai a matsayinta na mai shiga tsakani kai tsaye tsakanin Tehran da Washington ta gabatar da bukatarta na farfado da yarjejeniyar nukiliya inda Iran ta bada amsa akai wanda bangarorin tattaunawa suka bayyana shi a matsayin mai ma’ana sosai.

Kasar Amurka ta kwashe makwanni kafin ta bada Amsa ga bukatar da Iran ta gabatar wanda yanzu haka Iran ke nazari akai.

Daga karshe Abdallahiyan ya fadi cewa Iran da gaske take wajen ganin an kulla yarjejeniyar mai dorewa sai dai za’a iya cimma yarjejeniyar idan Amurka ta yi a da ya dace kuma ta karfafa bakatun da aka gabatar mata.

342/