Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Talata

23 Agusta 2022

16:47:27
1300325

Mutane 43 Sun Mutu Wasu Da Dama Sun Jikkata Sakamakon Gobarar Daji A Aljeriya

Rahotanni da suka fito daga kasar Aljeriya sun bayyana cewa Akalla mutane 43 ne aka tabbatar da mutuwarsu sakamakon wutar daji da ta kama gadun daji dake Arewa maso gabashin kasar a yan kwanakin nan da suka gabata, kuma an cafke mutane 13 da ake zargi da hannu wajen kai harin Arzon da ya jawo jikkatar mutane 200 da mafi yawancinsu suna samu mummunar kuna.

Mahukumta a kasar sun bayyana cewa yanzu haka ma’aikatan kwana-kwana na ci gaba da gudanar da ayyukan jin kai na gano Gawawwakin wadanda abin ya shafa, da ake ganin akwai yi yuwa adadin wadanda suka mutu ya karu,

A duk lokacin Zafi Arewacin kasar Aljeriya na fuskantar matsalar gobarar daji sai dai wannan bala’in na kara yawa a kowacce shekara saboda canjin yanayi dake haifar da fari da tsananin zafi, masana sun dora alhakin nakasun da aka samu a kan karacin kayan aiki na kashe gobara da wadataccen ruwa da kuma rashin kula da gandun dajin.

342/