Zaben dai ya gudana ba tare da hatsaniya ba a wasu jihohin, yayin da a wasu kuma an samu kace-na-ce tsakanin wasu `yan takara.
Haka nan kuma wasu gwamnoni sun samu damar yin nasarar takara a karo na biyu, yayin aka samun sabbin fuskoki a wasu jihohin musamman wadanda wa’adi na biyu na gwamnoninsu ya kare.
Duk da cewa zabukan sun gudana lami lafia, amma kuma wasu daga cikin ‘yan takara da ba su yi nasara ba, sun koka kana bin da suka kira magudi ko kuma nuna musu fin karfi.
342/