Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Asabar

28 Mayu 2022

15:02:09
1261804

​Shugaban Kungiyar Tarayyar Afrila Ya Bukaci Kasashen Yamma Su Dagewa Zimbabwe Takunkuman Da SUka Dora Mata

Shugaban karban karba na kungiyar tarayyar Afirka (AU), kuma shugaban kasar Senegal Macky Sall ya yi kira ga kasashen yamma da su kawo karshen takunkuman tattalin arzikin da suka dorawa kasar Zimbabwe kimani shekaru 20 da suka gabata.

Shafin yanar gizo na Labarai ‘Afirka news’ ya nakalto Sall yana fadar haka a jawabin bude taron da ya gabatar a birnin Malabo na kasar Equatorial Guinea, inda kungiyar AU take gudanar da taronta na farko kan agaji a mahiyar Afirka.

Kafin haka dai shugaban kasar Equatorial Guinea’ Teodoro Obiang ne ya bude taron a matsayin kasa wacce ta ke daukan bakwancin manya-manyan tarurruka guda biyu. Dukkaninsu dangane fa yadda za’a shafi kan matsalar ‘yan gudun hijira da kuma ayyukan bada Agaji a nahiyar,

Shugaba Sally a yi alkawar bada dalar Amurla miliyon uku a matsayin tallafin kasar kan wannan lamarin.

An kiyasta cewa yawan yan gudun hijira a nahiyar Afirka a shekara ta 2020 ya kai miliyon 282 kuma akwai has ashen cewa wannan adadin zai kara a wannan shekara da ake fada da karancin abinci a duniya gaba daya saboda yaki a Ukrain da kuma matsalolin cutar Corona suka jawo.

342/