Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Laraba

25 Mayu 2022

18:12:51
1260906

​Turkiya: Kamfanin Dillancin Labaran Turkiya Zai Yi Musayan Labarai Da NAN Na Najeriya

A yau laraba ce kamfanin dillancin labaran gwamnatin kasar Turkiyya Anadolu ya rattaba hannun kan yarjejeniyar musayar labarai da kamfanin dillancin labaran gwamnatin Najeriya NAN a kasar Turkiyya.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - NAN ya ce an rattaba hannu kan wannan yarjejeniyar ce a gefen taron kafafen yada labarai na Afirka da kasar Turkiya.

Labarin ya kara da cewa babban daraktan kamfanin dillancin labarai na NAN Mr Buki Ponle ne ya sanya hannu a madadin kamfanin, a yayinda Serdar Aragoz shugaban kwamitin gudanarwa da kamafanin Anadolu ya sanya hannu a madadin kamfaninsa.

An kafa Anadolu a shekara 1920 a birnin Ankara babban birnin kasar Turkiya, a yayinsa aka kaf NAN a shekara 1976 sannan ya fara aiki a shekara 1978.

Kamfanonin biyu zasu yi musayan labarai da harshen turanci, bidiyoyi da kuma hotuna a tsakaninsu.

342/