Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Alhamis

19 Mayu 2022

18:53:25
1259037

​Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Yarjejeniyar Nukiliya Da Yakin Ukraine

Ministan harkokin wajen Rasha Sergei Lavrov ya tattauna ta wayar tarho da takwaransa na Iran Hossein Amir Abdollahian kan batutuwa na kasa da kasa, ciki har da tattaunawa kan yiwuwar ci gaba da yarjejeniyar nukiliyar.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - A cikin wata sanarwa da ma'aikatar harkokin wajen kasar Rasha ta fitar, ta tabbatar da cewa, Lavrov da Abdollahian, a yayin tattaunawar da ta gudana a tsakaninsu a yau Alhamis, bisa shawarar da bangaren Iran ya gabatar, sun mayar da hankali ne kan muhimman batutuwan da suka shafi huldar kasashen biyu, da kuma yadda za a cimma matsaya.

Baya ga haka kuma, da komawa ga aiwatar da cikakken shirin hadin gwiwa kan shirin nukiliyar Iran ta 2015 tsakanin Tehran da gungun P5+1.

Ministocin biyu sun kuma yi musayar ra'ayi, a cewar sanarwar ta Rasha, kan wasu batutuwan gaggawa na yankin da kuma na kasa da kasa, ciki har da sabbin abubuwan da suka faru a halin da ake ciki a Ukraine, inda Moscow ke ci gaba da aikin soja.

342/