Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Laraba

18 Mayu 2022

19:28:30
1258757

Kasashen Iran Da Ghana Za su Kara Fadada Dangantakar Dake Tsakaninsu .

Ministan yawon bude Ido da aladu na kasar Ghana da ya jagoranci wata tawaga zuwa nan kasar iran domin halartar taron kwamitin hadin guiwa tsakanin Iran da Ghana karo Na 7 ya gana da ministan harkokin wajen kasar Iran Amir Abdollahiyan kuma dukkan su sun bayyana a niyarsu ta fadada dangantakar dake tsakaninsu a bangarori daban-daban.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - A lokacin ganawar tasu ministan waje na iran ya mayar da hankali sosai game da muhimmancin karfafa dangantakar dake tsakaninsu da kuma yin aiki da yarjejeniyoyin da aka cimma matsaya a kai, don haka za’a aike da tawagar Iran zuwa kasar Ghana domin fitar da taswirar tsarin dangantaka tsakanin kasashen biyu

Da yake tsokaci game da irin damar da iran take da shi a bangaroyin lafiya ,Noma, masana’antu, Ilimi, kimiya da fasaha da ayyukan injiniya da fada da Taa’danci da tsattsauran ra’ayi ministan ya nuna shirin kasarsa na yin aiki tare da kasar Ghana a dukkan wadannan bangarorin.

Anasa bangaren Mohammad Awal yayi ishara game da muhimmancin kara karfafa dangantaka tsakanin kasashen a bangaren sufurin jirgin ruwa da na sama, da kuma samar da layi jirgin sama kai tsaye zuwa kasar Ghana domin bunkasa harkokin yawon bude ido, masana’antu musamman yawon bude Ido na neman lafiya.

342/