Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Talata

17 Mayu 2022

19:32:40
1258436

​Iran: Amurka Da Qatar Sun Tattauna Batun Shirin Nukliyar Iran

Ministan harkokin wajen kasar Qatar ya tattaunawa ta wayar tarho da tokwaransa na kasar Amurka dangane da inda aka kwana a tattaunawar shirin nukliyar kasar Iran.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - kasar Iran ya nakalto kamfanin dillancin labaran kasar Qatar (QNA) yana fadar haka ya kumakara da cewa Mohammad bin Abdul Rahman Al Thani da Antony Blinken sun tattauna dangane da yaki a Ukrain, Afganistan da kuma dangantaka tsakanin kasashen biyu.

Wannan tattaunawar dai tana zuwa ne kwanaki bayan da sarkin kasar Qatar ya kawo ziyarar aiki a nan Tehran. Har’ila yau kafin haka Mohammad bin Abdul Rahman Al Thani ya tattauna da jami’a mai kula da al-amuran harkokin waje na kasar Kasar Josept Borrell da kuma Robert Mali jami’a mai kula da al’amuran kasar Iran na gwamnatin shugaban Biden kan batun.

342/