Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : hausatv
Lahadi

8 Mayu 2022

15:07:50
1255810

​Najeriya: Gwamnatin Tarayya Ta Roki Kamfanonin Jiragen Sama Da Kada Su Dakatar Da Ayyukansu

Gwamnatin tarayyar najeriya ta yi kira ga kamfanonin jiragen sama na cikin gida da su sake duba matakin da suka dauka na dakatar da ayyukansu saboda tashin farashin man Jet A1, wanda aka fi sani da man jiragen sama.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Hakan na zuwa ne sa’o’i kadan bayan da kamfanonin jiragen suka bayyana shirin dakatar da ayyukansu daga ranar Litinin 9 ga watan Mayun 2022, saboda tsadar man jiragen da ya tashi daga Naira 190 kan kowace lita zuwa Naira 700, ya haifar da matsaloli masu yawa ga kamfanonin jiragen.

Wannan bayanin na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman kan harkokin jama’a ga ministan sufurin jiragen sama, James Odaudu, ya fitar a ranar Asabar, inda ministan ya bukaci kamfanonin jiragen sama da su yi la’akari da illolin da matakin zai haifar, tare da nuna damuwarsa kan karuwar farashin man jirgin sama.

342/