Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Asabar

7 Mayu 2022

19:09:48
1255507

​Najeriya: Hukumar EFCC Zata Sanya Ido Kan Hanyoyin Samun Kudaden Yan Siyasa A Zaben Shekara Mai Zuwa

Shugaban hukumar yaki da ta’annuti wa tattalin arziki kasa a Najeriya Abdulrasheed Bawa ya bayyana cewa hukumarsa tare da hadin kai da hukumar zaben kasar zata sanya ido kan halaccin kadaden da ‘yan siyasa suke kashewa a harkokin zaben shekara mai zuwa. Bawa ya bayyana haka ne a harirar ta ta hada shi ta tashar Talabijon ta “Chbannel” a shirinta na “Politics Today” a jiya jumma.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Bawa ya kara da cewa hukumarsa zata bi duddugin dukkan kudaden ‘yan siyasa suke kashewa don hawa kan kujerun shugabanci daban daban a kasar, daga ciki har da kudaden sayan fom na takarar zabe daga na majalisar wakilai da har zuwa shugaban kasa.

Kafin haka dai yawan kudaden sayan fom na shiga takarar shugaban kasa, musamman a jam’iyya mai mulki APC da kuma PDP babban jam’iyyar adawa ya jawo korafe-korafe da dama a cikin mutanen kasar.

Labarin ya kara da cewa Jam’iyyar APC mai mulki ta sanya Naira miliyon 100 a matsayin farashin sayan fom don shiga takarar shugabancin kasa, sannan PDP kuma ta sanya naira miliyon 40 don sayan fom kawai. Daga karshe bawa ya kammala da cewa suna sun hana gurbatattun yan siyasa rike mukamai a kasar.

342/