Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Laraba

4 Mayu 2022

19:00:08
1254553

Dakarun Sojin Kasashen Armeniya Da Azarbaijin Sun Yi Musayar Wuta A Tsakaninsu

Rahotanni dake fitowa daga birnin baku sun nuna cewa an yi musayar wuta tsakanin sojojin kasar Azarbaijan da Armeniya a wani yankin dake iykokin kasashen guda biyu, rikici tsakanin kasahen biyu kan yankin Nagorno –Karabakh ya samo Asali ne tun a shekara ta 1988 kafin daga bisani ya rikide ya koma na soji a shekara ta 1992 bayan da sojojin kasar Armeniya suka mamaye yankin Nagorno- Karabakh da wasu ynkuna 7 na Jamhuriyar Azarbaijan dake makwabtaka da ita.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - A shekara ta 2020 kasar Armeniya ta gwabza fada da jamhuriayr Azarbaijan a karo na biyu kan hakkin ikon mallakar Nagorno- Karabakh sai dai an kawo karshen yakin bayan kwanaki 44 bayan da kasar rasha ta shiga tsakanin inda aka rattaba hannun kan yarjejeniyoyi guda 3 da ake kira da tripartite

A daren jiya ne kasar Azarbaijan ta sanar cewa an kai hark an sansanin sojojinta dake iyakar tad a Armeniya shi ma a nasa bangaren ministan tsaron kasar Armeniya ya fadi cewa sojojin Azarbaijan suk kai hari kan sansanin sojojinta da gangan, a garin Zilki dake yankin Kalbajar, da suka yi amfani da kananan makamai , sai dai tuni dakarunsu suka mayar da martani, amma babu Karin haske game da wadanda suka rasa rayukansu ko kuma suka jikkata ko asarar dukiyoyi

Jamiyun adawa a kasar ta Aremeniya sun zargi fira ministan kasar Nikol Pashinyan da kokarin mika yankin na Nagorno –Karabakh ga kasar Azarbaijan..

342/