Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Asabar

12 Maris 2022

13:46:26
1238430

Rasha Ta Zargi Amurka Da Taimakawa Kasar Ukiraniya Akan Yadda Za Ta Hada Makamai Masu Guba

Wakilin kasar Rasha a MDD Vasily Alekseevich Nebenzya ya bayyana cewa; A Karkashin Umarnin kasashen turai ne kasar Ukiraniya ta fara shirin samar da makamai masu guba,kuma tana kokarin boye wannan shirin nata.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Wakilin na kasar Rasha a MDD ya cigaba da cewa; Da akwai jerin dakunan bincike 30 akan makamai masu guba a fadin kasar Ukiraniya, da su ka kunshi yadda za a samar da cutuka masu hatsari, tare da yin gargadin cewa za su iya fadawa a hannun ‘yan ta’adda.

A jiya Juma’a ne dai kwamitin tsaro na MDD ya yi zama na musamman bisa bukatar Rasha, domin a tattauna yadda Amurka ta taimakawa Ukiraniya wajen kafa dakunan bincike na samar da cutuka masu hatsari da suka hada da kwalara da wasu cutuka.

Jakadan na kasar Rasha a MDD ya kuma ce; Amurkan tana son yin amfani da tsuntsayen jemage wajen yada cutukan akan iyakar kasar Rasha.

Tun da fari, kasar Rasha ta sanar da kama dakunan bincike na kimiyya masu yawa a cikin kasar Ukiraniya wadanda ta ce Amurkan tana amfani da su wajen samar da cutuka.

342/