Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Alhamis

24 Faburairu 2022

14:38:59
1233062

Kwamitin Tsaro Na Majalisar Dinkin Duniya Ya Gudanar Da Taron Gaggawa Karo Na Biyu Kan Rikicin Ukraine

Mambobin kwamitin tsaro na Majalisar dinkin duniya suna shirye shiryen fitar da daftarin kuduri game da kasar Ukrain , inda suka soki kasar Rasha game da matakin da ta dauka kan makwabciyarta, sai dai da dukkan alamu mataki ba zai yi nasara ba.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - A jiya laraba ce ministan harkokin wajen kasar Ukrain Dmytro Kuleba ya bukacin kwamitin tsaro na majalisar dinkin duniya day a kira zaman gaggawa saboda bukatar da yankunan Donetsk da Luhansk suka mikawa mahukumtan rasha na aikewa da sojoji saboda yadda yanayin tsaro yake kara tabarbarewa a wajen

An kara samun takun saka ne bayan da Amurka ta zargi kasar Rasha da aikewa da sojojinta 15,000 a kusa da iyakar kasar, domin kai mata hari da mamayeta, kuma an zargi Amurka da kawayenta da nuna damuwa kan lamarin.

342/