Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA -nakalto Le-Darain yana fadar haka bayan taron tattaunawa tsakanin kasashen da suke da sojojinsu a kasar Mali da kuma wasu manya manyan kasashen yamma a jiya Litinin ta hotunan bidiyo.
Ministan ya ce babu bukatar faaransa ta ci gaba da ajiye sojojinta a kasar Mali, don babu fahintar juna da gwamnatin sojojin da suke iko da kasar a halin yanzu.
Labarin ya kara da cewa a gobe Laraba ce ake saran shuwagabannin ragowar kasashen Sahel 3 wato Niger, Chadi da Mauritani zasu gudanar da taro kan matsalar ta Mali. Har’ila yau an gayyaci Najeriyacikin a taron na gobe. Amma banda Mali da Burkina Faso.
342/