Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Kasar Amurka ta sanar da dage takunkumi kan shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya, a matsayin wani mataki na nuna aniyarta ta dawowa cikin tattaunawar da aka kulla yarjejeniya a kai a shekara ta 2015.
Anasa bangaren kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Saed Khatib Zade ya fadi cewa iran dama tana jiran Amurka ta cika alkawuran da ta dauka da kuma aiki da nauyin da ya rataya a wuyarta na cirewa iran takunkumi , yace abin da ya fi dacewa shi ne Amurka ta cire dukkan takunkumin da ta kakabawa kasar Iran,
342/