Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Asabar

5 Faburairu 2022

18:35:36
1226298

​Iran: Amurka Ta Dagewa Iran Wasu Takunkuman Da Suka Shafi Ayyukan Nukliya

Gwamnatin kasar Amurka ta dangewa Iran wasu takunkuman wadanda suka shafi ayyukan Nukliya na zaman lafiya a kokarin da take yi na kodaitar da ita ta koma kan mutunta yarjejeniyar JCPOA ta shekara 2015 wacce Amurka da fice a shekara ta 2018.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Associated Press ta bayyana cewa gwamnatin Biden ta yi haka ne don ganin an gaggauta kammala tattaunawa da take gudana a halin yanzu a birnin Vienna na kasar Astria na dagewa Iran dukkan takunkuman da Amurka ta dora mata bayan ficewar ta daga yarjejeniyar kimani shekaru 4 da suka gabata.

Gwamnatin Biden dai ta ce tana son dawowa cin yarjejeniyar amma tana jan kafa wajen dawowar saboda tana son samun lamuni daga Iran kan wasu al-amura. Sai dai gwamnatin Iran ta dage kan dole ne Amurka ta dage dukkan takunkuman da aka dora mata tun bayan ficewarta daga yarjejeniyar.

342/