Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Alhamis

20 Janairu 2022

09:59:13
1220662

EU: Bata Son Maida Kasar Mali Saniyar Ware, Amma Ta Dawo Kan Turbar Democradiyya

Jakadan kungiyar tarayyar turai a yankin Sahel ya bayyana cewa kasashen tarayyar EU basa son maida kasar Mali saniyar ware, amma kofar tattaunawa da ita a bude take idan sojoji masu juyin mulkin kasar sun amince.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Kamfanin dillancin labaran reuters ya nakalto Emanuela Del Re yana cewa kungiyar ta EU tana shirin karawa kasar ta Mali takunkuman tattalin arziki a bangarenta idan ta ki gudanar da zabubbuka kamar yadda aka tsara.

Kafin haka dai sojojin masu juyin mulki a kasar ta Mali sun dage shirin mika mulki ga fararen hula a farkon wannan shekarar da muke ciki, zuwa wasu shekaru 4 masu zuwa. Kasar Mali wacce take fama da tashe-tashen hankula tun bayan juyin mulki na shekara ta 2012, ta ce ta dage lokacin zaben ne don matsalolin tsaron da kasar take fama da su.

Kasar Faransa tana da dubban sojojin a kasar Mali tun shekara ta 2013 da sunan yaki da yan ta'adda, amma tun lokacin 'yan ta'addan sai kara karfi suke.

342/