Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Talata

21 Disamba 2021

13:24:33
1210829

​MDD Ta Yi Gargadi Game Da Barazanar Fari A Somaliya

Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadi game da barazanar fari dakan iya shafar dubban mutane a Somalia.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti{a.s} - ABNA - Akalla mutum daya cikin hudu ne ke fuskantar barazanar yunwa a Somaliya a sabili da fari da kasar ke fuskanta a cewar Majalisar Dinkin Duniya a wani rahoton gargadin da ta fitar.

Wannan dai na zuwa ne bayan karancin ruwan saman da kasar ta fuskanta na kusan damina hudu a jere.

A cewar rahoton matsalar za ta yi kamarin da za ta kai ga barin kusan mutum miliyan 5 ga bukatar agajin gagawa na abinci.

Sama da shekaru 30 Somaliyar bata taba fuskantar irin wannan hali na fari da ta shiga ba.

A watan da ya gabata mahukuntan Somaliya suka ayyana wannan matsala ta fari a matsayin abun damuwa dake bukatar tallafin gaggawa.

342/