Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Litinin

20 Disamba 2021

16:33:22
1210520

​Faransa Ta Ce Za Ta Binkici Kisan Da Ake Zargin Sojojinta Da Aikatawa A Nijar

Ma’aikatar tsaron kasar Faransa, ta ce su na gudanar da cikakken bincike a kan abin da ya haddasa mutuwar wasu mutum uku yayin boren da akayi wa dakarun kasar a yankin Tera na Jamhuriyar Nijar cikin watan jiya.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti{a.s} - ABNA - A ranar Juma'a ne cikin jawabin da ya yi a jajibirin bikin cika shekara 63 da kasar ta zama Jamhuriya, Shugaba Mohamed Bazoum na Nijar, ya yi kira ga faransa da ta gudanar da bincike a kan mutuwar masu zanga zangar, lokacin da ayarin dakarunta ke kan hanyarsu ta zuwa Mali.

Ministar tsaron kasar Faransa, Florence Parly, ta ce sojojin kasar sun yi iya kokarin ganin sun yi abin da ya dace a lokacin yamutsin.

Ministar ta kuma ce ana ci gaba da tattaunawa a kan batun da mahukuntan Jamhuriyar Nijar.

342/