Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Litinin

20 Disamba 2021

16:21:09
1210512

Faransa Ta Jinjinawa Sojojinta Da Suka Kashe Fararen Hula Bayan Taho Mu Gama A Niger

Ministan tsaro na kasar Faransa Florence Parly ya fadi cewa sojojin kasar sun gudanar da binciken cikin gida game da taho mu gama da aka yi tsakaninsu da wasu fararen hula a Kasar Niger da yayi sanadiyar mutuwar mutane 3,

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti{a.s} - ABNA - Binciken yana zuwa ne bayan shugaban kasar Niger mohammad Bazoum ya bukaci a gudanar da bincike kan ayarin sojojin Faransa dake hanyarsu ta zuwa kasar mali da ya haddasa zanga-zanga da ta jawo asarar rayuka.

Akalla mutane 2 ne suka mutu wasu guda 18 kuma suka jikkata bayan da tawagar sojojin Faransa ta budewa huta domin tarwatsa masu zanga-zanga da suka tsare musu hanya a yammacin kasar Niger.

Ana ta bangaren kakakin sojojin kasar Faransa Pascal Lanni ya fadi cewa: “babu wani sojojin Faransa daya jikkata sakamakon taho mu gamar, sai dai wasu fararen hula guda biyu sun jikkata bayan da aka jefesu da duwatsu.

Daga karshe ta bayyana cewa suna ci gaba da tattaunawa da gwamnatin Niger domin gano hakikanin abin da ya faru kafin da lokaci da kuma bayan afkuwar hargitsin.

342/