Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Alhamis

16 Disamba 2021

13:24:28
1209233

​Gwamnatin Faransa Na Shirin Janye Kaso Mai Yawa Na Dakarunta Daga Yankin Sahel

Babban Kwamandan Rundunar sojin Faransa ta Bakhan a yankin Sahel Janar Laurent ya ce, Faransa za ta rage dakarunta a yankin Sahel zuwa dubu 3 sabanin dubu 5, nan da wasu 'yan makwanni, a karkashin babban garanbawul din da take yi wa rundunar sojojinta a yankin kamar yadda babban Kwamandan Rundunar Yaki da 'Yan ta’adda ta Barkhane.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti{a.s} - ABNA - A rahoton da kamfanin dillancin labaran AFP ya bayar, dangane da burin sake fasalta rundunar sojin Faransar a yankin Sahel a 2022 mai shirin kamawa, Babban Kwamandan Rundunar ta Bakhan Janar Laurent Michon ya bayyana cewa, suna kan mataki na karshe ne, abin nufi shi ne na janye sojojin da ke yankin arewacin kasar Mali a garuruwan Tombouctou, Kidal, da Tessalit), a wasu lokutan aikin na tafiya ne tare da sa hannun mahukuntan Mali, da kuma na rundunar Majalisar Dinkin Duniya a Mali Minusma, sai kuma aminai na rundunar hadin guiwar kasashe.

Janye dakarun da ke tafiya mataki-mataki na tafiya dai dai kamar yadda aka tsara.

A wannan fage da aka raba tsakanin rundunar Faransa da ta dakarun Majalisar Dinkin Duniya Minusma, alakar za ta ci gaba da tafiya ne ba canji domin dakarun Mali ne za su canji sojin na Faransa a cewar kwamandan na dakarn Faransa.

Zango na biyu na janye dakarun kuma, zai fara a cikin watanni 3 masu zuwa.

342/