Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti{a.s} - ABNA- Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Ministan kiwon lafiya na kasar Burtaniya Sajid Javid yana fadar haka a jiya Asabar.
Kafin haka dai firai ministan kasar ta Burtaniya Boris Johnson ya bayyana cewa gwamnatinsa ta dauki tsauraran matakai kan matafiya masu shigowa kasar ne don tabbatar cewa cutar Covid 19 nau’in Omicron wacce ake bincike a kanta a halin yanzu bata yadu a kasar ba.
Har’ila yau cibiyar kula da harkokin lafiya ta kasar ta bada sanarwan cewa, ya zuwa yanzu an sami mutane 160 na wadanda suka kamu da sabuwar Covid 19 nau’in na Omicron a kasar ta Burtania.
342/