Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {A.S} - ABNA : Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto Hans Kluge wani masani na hukumar lafiya ta duniya ya na fadar haka, ya kuma nuna damuwarsa da yadda cutar take kara yaduwa a kasashen na Turai, sannan ya bukaci gwamnatocin kasashen nahiyar, musamman na kasashen Jamus da Austria da su dauki matakan tilastawa mutanensu sanya takunkuman rufe baki, wanda zai iya yin tasiri wajen rage saurin yaduwar cutar a kasashen nasu.
KlugeCalugeh ya kara da cewa, zuwan fasalin sanyi, da kuma samuwar nau’in cutar ta Delta ya kara saurin yaduwarta a cikin wadannan kasashe, don haka dole ne a dauki matakan kiwon lafiya masu tsanani sannan kara sauri wajen yiwa mutane alluran riga kafin cutar saboda dakile ta.
342/