Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : hausatv
Asabar

13 Nuwamba 2021

16:34:35
1198130

​Amurka: ‘Yar Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Bukatar A Hana Sayarwa Saudiya Makamai

‘Yar majalisar dokokin kasar Amurka Ilham Omar ta gabatar da wata bukata ga majalisar wakilan kasar ta neman gwamnatin shugaban Biden ta dakatar da cinikin makamai masu linzami wadanda ta sayarwa kasar saudiya saboda kissan kiyashen da takewa mutanen kasar Yemen da kuma ayyukanta na take hakkin bil’adama.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {A.S} - ABNA : Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Omar tana fadar haka a jiya Jumma’a ta kuma kara da cewa majalisar dokokin kasar Amurka tana da karfin hana wannan cinikin, kuma Amurka bai kamata ta saida makamai ga kasashen da suke take hakkin bi’adama ba.

Labarin ya kara da cewa wannan bukatar ta Omar ta zo ne a lokacinda Amurkawa da dama suke nuna damuwarsu da irin yadda gwamnatin kasar Saudia take kissan mutanen kasar Yemen.

A ranar 4 ga watan Nuwamban da muke ciki ne gwamnatin shugaba Biden ta bada sanarwan cewa ta sayarwa kasar Saudiya karin makamai masu linzami wadanda ake cillasu daga sama zuwa kasa har 280 a kan kudi dalar Amurla miliyon $650.

342/