Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : hausatv
Asabar

18 Satumba 2021

12:14:09
1180975

Iraki: Wani Dan Majalisar Kasar Ya Ce Amurka Zata Fara Janye Sojojinta Daga Kasar A Cikin Wata Mai Kamawa

Wani dan majalisar dokokin kasar Iraki ya bada sanarwan cewa gwamnatin kasar Amurka zata fara janye sojojinta daga kasar a cikin watan Octoba mai zuwa, kuma kafin karshen wannan shekarar zata janye dukkan sojojinta daga kasar.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {A.S} - ABNA : kasar Iran ya nakalto Badr Zayidi mamba a kwamitin tsaro na majalisar dokokin kasar ta Iraki yana fadar haka a jiya Alhamis, ya kuma kara da cewa ficewar sojojin Amurka daga kasar Iraki yana zuwa ne bisa yarjejeniyar da Amurkan da cimma da gwamnatin Mustafa Al-kazimi a ckin watan Yunin da ya gabata.

Labarin ya kara da cewa a halin yanzu akwai sojojin Amurka kimani 2500 a cikin kasar Iraki, sannan zuwa ranar daya ga watan Jenerun shekara ta 2022 ba wani sojoan Amurka da zai rage a kasar, sai wadanda zasu ci gaba da horas da sojojin kasar da kuma bada shawara.

342/