Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {A.S} - ABNA : Tallafin ya samu ne bayan taron kasa da kasa da aka gudanar ranar Litini a Geneva domin samar wa da kasar ta Afghanistan tallafi.
Babban sakataren MDD, Antonio Guteress, ya yi fatan tallafin zai taimaka wajen ayyukan kare hakkin dan adam a wannan kasa ta Afghanistan.
Kimanin ‘yan Afghanistan miliyan 11 ne ke bukatar tallafin jin kai a cewar MDD.
Mista Guteress, ya bukaci da a tattauna da kungiyar Taliban dake mulki a kasar, saboda a cewarsa ba yadda za’a shayo kan halin da ake ciki a kasar ba tare da damawa da ‘yan Taliban ba.
‘’Ya kuma babu wata riga ga kakaba wa kungiyar Taliban takunkumi’’.
342/