Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti{A.S} - ABNA : Labarin ya kara da cewa an cilla makaman rokan ne da misalin karfe 8 na yammacin jiya Talata, kuma harin ya haddasa asarorin dukiya masu yawa amma babu labarin ko akwai asarar rayuka.
Majiyar ta kara da cewa mayakan kungiyoyin ‘yan ta’adda masu samun mafaka a cibiyar sun rikice.Banda haka wata majiya ta bayyana cewa makaman sun taso ne daga yankunan da sojojin Siriya suke iko da su a yankin, jiragen yakin kawancen sun yi ta shawagi daga bayan a kan yankin har zuwa tsakiyar dare, amma babu labarin kai farmaki ko luguden wuta a wani wuri a yankin.
Cibiyar kawancen Amurka da sunan yaki da kungiyar ‘yan ta’adda ta Daesh dai ba bisa ka’ida aka kafa ta ba, don bata sami izinin gwamnatin kasar Siriya ba.
342/