Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : hausatv
Litinin

30 Agusta 2021

12:54:17
1174858

​Iran Ta Ce Za Ta Maida Martani Na Daban Ga Barazanar Amurka Da Isra’ila Gare ta

Wani babban jami’in tsaro na kasar Iran ya bayyana cewa barazanar Amurka na cewa za ta yi amfani da wani zabin, wanda yake nufin yaki, idan har zabin diblomasiyya bai kai ta ga burinta a kan kasar ba, zai gamu da maida martani ko kuma kare kanta da ‘wani zabin’ ita ma.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti{A.S} - ABNA : Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban Biden na kasar Amurka ya na fadar haka a lokacinda yake ganawa da sabon Firai ministan haramtacciyar kasar Isar’ila (HKI) Naftali Bennett a washingtong a jiya Asabar.

Jami’in ya kara da cewa zabin diblomasiyya a wajen Biden shi ne ‘tattaunawar Vienna a kasar Austria’ dangane da komawar Amurka cikin yarjejeniyar JCPOA, sannan wasu zabin kuma ya na nufin yaki ne, idan tattaunawar Vienna ta kasa tilastawa Iran amincewa da bukatunta.

Iran dai ta bayyana cewa ba za ta amince da komawa kan yarjejeniyar JCPOA ba, sai idan Amurka ta dauke dukkan takunkuman da gwamnatin Trump ta dorawa kasar bayan ya fitarda kasar daga yarjejeniyar ta JCPOA a shekara 2018.

342/