Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti{A.S} - ABNA : Da yake sanar da hakan ranar Asabar, bayan ganawa da mashawartansa kan harkokin tsaro, Mista Biden, ya kara da cewa, har yanzu akwai babbar barazana da kuma yiwuwar fuskantar hare haren ta’addanci a filin jirgin saman na Kabul.
Game da harin da Amurka ta kai a gabashin Afghanistan kuwa inda ta kashe wasu mambobin kungiyar IS biyu, shugaba Biden, ya ce harin ba zai zamo na karshe ba.
A harin ta sama data kai jiya Asabar, rundunar sojin Amurka ta ce, ta hallaka wani jigon kungiyar IS da ya kitsa yadda aka kai harin filin jirgin saman Kabul.
Harin kunar bakin waken na ranar Alhamis ya kashe mutun 170 da suka hada da sojojin Amurka 13.
342/