Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti{A.S} - ABNA : Amurka ta kakabawa kasar takunkumin karya tattalin arziki daban daban domin durkusar da gwamnatin Nicola Madoro tare da maye gurbinsa da shugaban Yan adawa na kasar Juan Guido, takunkumin ya kun shi kwace kadarorin kasar da ke kasashen waje ba bisa ka’ida ba, da kuma toshe tattalin Arzikin kasar da hakan ya jefa miliyoyin mutanen kasar cikin mawuyacin hali.
A watan Fabarerun shekara ta 2020 gwamnatin kasar ta kai karan Amurka gaban kotun ICC in da ta bayyana matakin da Amurka ta ke dauka a kanta a matsayin cin zarfafin dan Adam, Wakilan gwamnatin Kasar da na ‘Yan adawa suna tattaunawa a kasar Meziko domin gano hanyoyin warware matsalar tattalin arziki da siyasa da kasar ke ciki.
342/