Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti{a.s} - ABNA : Kamfanin dillancin labaran Reuters ya bayyana cewa a halin yanzu asbitocin kasar a cike suke da wadanda suka ji rauni sanadiyyar girgizar kasar, wanda yawansu ya kai 5,700.
Tuni dai gwamnatin kasar Ta Haiti ta bukaci taimako daga kasashen duniya, don jinyan wadanda suka ji rauni. Labarin ya kara da cewa a arewa maso yammacin garin Jeremia likitoci suna jinyar wadanda suka ji rauni karkashin itatuwa, ko a kan tatifa a kasa saboda cikar asbitocin kasar.
342/