ABNA24 : Kalamman na Mista Ghani, na zuwa ne a daidai lokacin da mayakan Taliban ke matsa kaimi kan wasu manyan biranen kasar, a daidai lokacin da kuma sojojin na Afganistan ke kara azama wajen kwato yankunan dake hannun Taliban.
Rikici ya ta’azzara a kasar ne a farkon watan Mayu, lokacin da kungiyar Taliban ta kaddamar da munanan hare hare yayin da sojojin kasashen waje dake karkashin jagorancin Amukra ke kokarin kammala ficewa daga kasar.
A karshen watan Agusta nan ne Amurka ta ce za a karkare janye dakarunta daga kasar ta Afghanistan.
Shugaba Joe Biden na Amurka dai, ya bayyana ranar 11 ga watan Satumban 2021 din nan a matsayin ranar janye ragowar dakarun kasar daga Afghanistan bayan shafe shekaru 20 suna gwabza yaki da mayakan Taliban da na Al’Qaeda.
342/