ABNA24 : Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto wata majiya ta kasar Amurka ta na cewa Amurka zata daukar dukkan matakanda ta ga sun dace, don kare kawayenta a bangaren kudancin duniya.
Labarin ya kara da cewa jiragen ruwa dauke da makamai guda biyu ne a halin yanzu suke daba da isa kasashen don isar da makaman da kasashen biyu suka saya daga kasar Iran tun a zamanin tsohon shugaban Amurka Donal Trump.
Gwamnatin Amurka dai bata yarda da Nicolas Maduro a matsayin shugaban kasar Venezuela ba, kuma ta sha yunkurin kifar da gwamnatinsa amma ba tare da samun nasara ba. Kasar Cuba kuma tana karkashin takunkuman Amurka tunshekara 1959.
342/