ABNA24 : Hare haren na baya bayan nan su ne mafi muni a kasar, tun bayan soma rikici mai nasaba da gungun kungiyoyi masu ikirari da sunan jihadi a shekarar 2015.
A wata sanarwa da ta samu sa hannun kakakinsa, Stephane Dujarric, Guterres ya bayyana bacin ransa a game da kashe kashen daruruwan farar hula da suka hada da mata da yara.
Guterres ya caccaki wannan ta’asa, sannan ya jaddada bukatar kasashen duniya su rubanya goyon bayan da suke bai wa kasashen da ke fama da matsalar ta’addanci.
Babu dai wata kungiya da ta yi ikirarin kai harin.
342/