Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : hausatv
Lahadi

30 Mayu 2021

13:23:58
1145868

​Iran:Wasu Sanatoci Sun Bukaci Biden Ya Ci Gaba Da Dorawa Iran Takukunan Tattalin Arzikin Da Gwamnatin Trump Ta Dorawa Kasar

Wasu sanatoci a majalisar dattawan kasar Amurka sun gabatar da wani kudurin doka wacce ta bukaci gwamnatin shugaban Biden ta ci gaba da dorawa kasar Iran takunkuman tattalin arziki mafi muni a tarihin kasar, wadanda gwamnatin da ta shude ta dora mata.

ABNA24 : Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyanan cewa dokar wacce sanata James Lankford, John Cornyn da kuma Tim Scott suka gabatar ta sami goyon bayan tsohon sakataren harkokin wajen kasar ta Amurla Mike Pompeo.

Dokar ta bukaci a ci gaba da dorawa kasar Iran takunkunman tattalin arziki mafi tsanani, har sai da dawo kan yarjejeniyar JCPOA sannan ta daina abinda suka kira shihsigi a cikin al-amuran kasashen kudancin Asia sannan da takatar da shirinta na makamai masu linzami.

Wadannan sanatoci dai sun kaddamar da wannan bukatarne a dai-dai lokacinda ake tattaunawa tsakanin kasshen da suka rage a yarjejeniyar ta JCPOA suke son dawo da Amurka cikinta.

Tuni dai gwamnatin shugaba Biden ta amince ta dage manya manyan takunkuman tattalin arzikin da aka dorawa kasar, wadanda suka hada da sayar da danyen man fetur da kuma Bankuna, amma Iran ta na bukatar fiye da haka nesa ba kusa ba.

342/