ABNA24 : Har ila yau tashar ta al-mayadeen din ta kara da cewa; Kasashen biyu suna shirin musayar fursunoni da su ka kunshi ‘yan leken asirin Amurka 4 da Iran take rike da su.
A lokacin gwamnatin Barrack Obama Iran ta sake wani dan leken asirin Amurka mai suna Jason Rezaian, bayan da Amurkan ta saki kudaden Iran da take rike da su a wancan lokacin da su ka kai dala biliyan daya da miliyan dari bakwai.
342/